Kamfanin dillancin labaran Ahlul-Baiti (ABNA) ya bayar da rahoton cewa: a cikin ‘yan mintoci da suka gabata kungiyar IRGC ta fitar da sanarwa inda ta sanar da kai hari kan cibiyoyin leken asiri na gwamnatin ‘yan ta’adda a yankunan da aka mamaye, tare da sanar da shahadar wasu jami’an leken asirin guda uku a sakamakon harin na gwamnatin sahyoniyawa.
Bayanin shi ne kamar haka:
انا من المجرمون منتقمون
Muna masu sanar da al'ummar Iran masu daraja cewa a yau sojojin gwamnatin sahyoniyawa azzalumi da rudu sun ci gaba da kai hare-hare da munanan ayyukan da suke yi wa Iran. Haka nan kuma ta sake bayyanar da mugunyar ta ta'addanci ta hanyar kai hare-hare ga masoya a wuraren zama tare da kashe wasu sojojin Gum Nam na Imamin Zamani (As) da kwamandojin mujahidan leken asiri, shahidai Mohammad Kazemi, Hassan Mohaqiq da Mohsen Bagheri.
Mayakan IRGC Aerospace Force, suna ci gaba da yin martaninsu mai murkushewa, musamman na daukar fansa kan laifuffukan da gwamnatin 'yan ta'adda suka aikata a yau, sun kai wani sabon hari na makamai masu linzami, inda suka kai hari kan cibiyoyin leken asiri na gwamnatin 'yan mamaya a matsayin kashi na uku na aikin Alkawarin Gaskiya 3.
Magoya bayan wannan gwamnatin ta muggan laifuka ya kamata su sani cewa za a ci gaba da gudanar da ayyuka masu inganci da niyya a kan muhimman wuraren wannan gwamnatin karyar har sai an ruguza ta.
ومن نصر الا من عندالله عزیز الحکیم
Your Comment